A Najeriya, jam’iyyar NNPP a jihar Kano, ta mayar wa APC mai barin gado martani game da kiraye-kirayen da take yi cewa hukumar zabe ta sake nazari kan sakamakon zaɓen gwamnan jihar da ya bai wa Abba Kabir Yusuf (Gida-gida) nasara a zaben da aka yi da ya ba shi nasara.
APC dai ta ce ba ta amince da sakamakon zaben ba kuma za ta garzaya kotu don kalubalantar su
To, sai dai shugaban jam’iyyar NNPP na Kano, Umar Haruna Doguwa ya ce duk masu bai wa Dr Nasiru Yusuf Gawuna shawarar ya je kotu to kuwa so suke ya yi biyu babu.

0 Comments